in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta jinjinawa aniyar Amurka ta cire Cuba daga kasashen dake goyon bayan ta'addanci
2015-04-15 20:15:05 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei, ya ce kasarsa na maraba da kudurun Amurka, na cire kasar Cuba daga jerin kasashen dake goyawa ta'addanci baya.

Mr. Hong ya ce rahoton dake kunshe da wannan aniya ta Amurka, ya nuna burin kasar na dinke barakar dake tsakaninta da Cuba. Matakin da kuma zai taimaka matuka, wajen inganta kudurin kasashen biyu na sake dawo da dangantakar diflomasiyya mai dorewa.

Mr. Hong wanda ya bayyana hakan yayin wani taron manema labaru da ya gudana a nan birnin Beijing, ya kara da cewa Sin na fatan ganin Amurka ta dage takunkumin da ta sanyawa Cuba, matakin da zai taimakawa bunkasar kasashen biyu, da al'ummunsu, da ma burin wanzar da zaman lafiya da ci gaban yankin da suke.

Kasar Cuba dai ta kasance cikin jerin kasashen da Amurka ke kallo, a matsayin masu goyon bayan ta'addanci a duniya tun cikin shekarar 1982. Sauran kasashen dake kan wannan layi su ne Iran, da Sham, da kuma Sudan. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China