in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya ta daskarar da ma'ajin hukumomin kudin kasar saboda alaka da ta'addanci
2015-04-08 21:04:59 cri
Gwamnatin kasar Kenya a ranar laraban nan ta buga sunayen hukumomi kungiyoyi da mutane 86 tare da daskarar da ma'ajin kudin hukomomin kudin 13 da ake ma zargin suna da alaka da ta'addanci a kasar.

A cikin sanarwar na ta mujallar gwamnati, an kuma bada umurnin ga duk bankuna dabankunan kananan masana'antu da kada su gudanar da huldarsu da wadanda aka lissafa ta tare da bada bayanai na duk wani wata mu'amala da aka yi da su ga babban bankin kasar cikin awowi 48.

Sakataren baitul malin kasar Kamau Thugge ya shaida ma manema labarai a Nairobi cewa gwamnati ta kuma dakatar da duk wani nau'in musayar kudi da alummar Somaliya.

Jerin sunayen dai yazo ne sakamakon harin da aka kai ga jami'ar Moi na garin Garissa a ranar alhamis din makon jiya inda aka hallaka mutane 148 sannan wassu sama da 70 suka ji rauni.

Wannan sanarwar gwamnatin da ya fara aiki tun daga ranar talata 7 ga wata ya lissafa sunayen kungiyoyin 'yan ta'adda da suka hada da Al shabaab, Boko Haram, IS na Iraqi da kuma ISIS na Sham sannan da MRC na Mombasa.

Sakataren jamalissar tsaron kasar Raychelle Omamo yace gwamnati ta riga ta dauki matakan kakkabe ta'addanci a doron kasar Kenya.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China