in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
shugaban majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya gana da shugaban majalisar wakilan kasar Habasha
2015-04-08 20:26:34 cri
Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Mr Zhang Dejiang ya gana da shugaban majalisar wakilan kasar Habasha Kassa Teklebirhan a yau Laraba 8 ga wata a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar tasu, Mr Zhang ya ce, Habasha ta kasance abokiya mai muhimmanci ga kasar Sin ta fuskar hadin gwiwa da kasashen Afrika, a cikin shekaru 45 da kafuwar dangantakar diplomasiyya tsakaninsu musamman ma a shekarun nan baya, shugabannin kasashen biyu na zurfafa mu'ammala tsakaninsu .

Sannan kuma inji Mr Zhang bangarorin biyu na samun ci gaba sosai ta fuskar yin hadin kai, hakan ya sa, dangantakar dake tsakaninsu ya zama abin koyi wajen hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. A don haka Majalisar wakilan jama'ar kasar Sin na mai da muhimmanci sosai wajen raya dangantakar dake tsakaninta da majalisar wakilan Habasha.

A nasa bangare, Kassa Teklebirhan ya ce, Habasha na mai da kasar Sin matsayin muhimmiyar abokiyar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, kuma tana fatan ci gaba da yin mu'ammala tsakanin manyan shugabannin kasashen biyu tare da tabbatar da matsaya daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma da kuma aiwatar da manyan ayyukan hadin gwiwa a tsakaninsu. Sa'an nan a habaka mu'ammala tsakanin jama'arsu da majalisun su.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China