in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shirin Amurka na sake tattaunawa da shugaba Asad na Sham
2015-04-16 15:43:24 cri

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka John Kerry ya sanar cewa, Amurka za ta nemi yin sulhu da gwamnatin kasar Sham a kokarin da take na ganin an kawo karshen tashin hankalin da aka shafe kusan shekaru hudu ana gwabzawa a kasar

John Kerry ya ce,tattaunawar Geneva da aka yi har sau biyu a watan Yunin shekara ta 2012 da kuma watan Janairun shekara ta 2014 duk ba su kai ga kawo karshen rikicin kasar ta Sham ba, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 220,000 kana fiye da rabin mazauna kasar aka tilasta musu tsere wa daga gidajensu,yayin da kusan mutane miliyan 4 ke gudun hijira a sansanonin 'yan gudun hijira dake kasashe makwabta.

Shirin gwamnatin Obama game da Sham yana zuwa ne sakamakon karin sukar da ya yake sha a gida da waje, ganin yadda a baya ya nace cewa, saukar da shugaba Assad daga mulki ne kadai mafita kan sulhunta batun kasar Sham, sai kuma yanzu ya yi shiru tun bayan da kasar ta kai hari a kan 'yan kungiyar IS a kasashen Iraqi da Sham a shekarar bara.

Masu sharhi na dora laifin rashin mutunta yarjejeniyar kan shugaban kasar ta Sham Bashar al-Assad wanda ya sa dukkan wadannan yarjejeniyoyi wargaje wa.Yanzu haka Amurka na kokari tare da sauran masu ruwa da tsaki don ganin an sake cimma wata mafita ta diflomasiyya, maimakon amfani da karfin soja.(Ibrahim/Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China