in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tsaurara tsaro a majami'un Garissa da kewaye sakamakon harin Al-Shabaab
2015-04-06 16:04:42 cri

A kasar Kenya majami'un garin Garissa da kewayensa, sun tsaurara matakan tsaro biyowa bayan harin da kungiyar Al-Shabaab ta kaiwa jami'ar Moi dake garin a ranar Alhamis din makon jiya.

Rahotanni sun nuna cewa an tsaurara matakan tsaro kwarai a lokutan addu'o'in da suka gabata a jiya Lahadi, bayan aukuwar wancan hari da ya yi sanadiyar rasuwar mutane 148. Wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ya rawaito cewa an girke a kalla jami'an tsaro 3 zuwa 6 a daukacin majami'u 36 dake garin Garissa.

A daya hannun kuma majami'un da a baya ke cika da mutane, a wannan karo sun samu karancin masu halartar abada, sakamakon tsoron abinda ka je ya zo. An bayyana cewa da dama daga mabiya addinin kirista a Garissa sun kasance a gidajen su, inda suke ci gaba da tattaunawa game da tasirin wancan hari, wanda ya zamo mafi muni a tarihin yankin. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China