in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan hanyoyin Ghana yana fatan masu saka jari na Sin za su tashi tsaye don gina muhimman ababen more rayuwa a Ghana
2015-04-01 15:40:52 cri


Kwanan baya, yayin da ministan dake kula da harkokin hanyoyi na jamhuriyar Ghana Alhaji A.B. Inusah Fuseini ke zantawa da wakilinmu, ya bayyana cewa, kasar Ghana tana maraba da masu saka jari na Sin da za su je kasar Ghana don gina manyan ababen more rayuwa a kasar, kuma Ghana za ta kokarta don taimaka musu idan za su bi dokokin kasar. Ya ce, a 'yan shekarun nan da muke ciki, Ghana ta samu matsaloli da dama dake shafar hanyoyi, yana fatan Sinawa za su tashi tsaye don taimakawa kasar. Sabo da ya taba jin karin maganar basine wai "Idan aka so samun ci gaba, dole ne a gina hanyoyi a farko."Yana sa ran ci gaba da hadin gwiwa da kasar Sin, don samun kwalliya biya kudin sabulu wajen raya hanyoyin kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China