Tun daga safiyar yau ranar 28 ga watan Maris, aka fara zaben shugabancin tarayyar Najeriya a duk fadin kasar. Tuni aka yi shirin gama aikin tantance matsayin masu kada kuri'a da misalin karfe 1 na yamma, sai a fara jefa kuri'a da karfe 1 da rabi. Amma a wasu sassan kasar, aka samu matsala kadan wajen amfani da na'urar zamani mai tantance matsayin masu kada kuri'a, wato "Card Readers" a turance. Wakilinmu Murtala ya zanta da wasu masu zuwa jefa kuri'a daga jihohin Lagos, Nassarawa da kuma Yobe ta waya, yanzu bari mu ji abun da suka fada.
150328babban-zaben-Najeriya-2015.m4a
|
150328murtala
|