in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin zata cigaba da bin tsarin kudin da ta fitar na taka tsantsan, inji Gwamnan babban bankin Kasar
2015-03-12 20:53:16 cri
Gwamnan babban bankin kasar Sin Zhou Xiaochuan a ranar alhamis din nan ya bayyana cewa kasar zata cigaba da rike tsarin kudin da ta fitar na taka tsantsan duk da sabbin manufofin da aka fitar, da wanda ake iya sauyawa koda yaushe domin shawo kan matsalar raguwar farashin kaya da ake iya fuskanta da sa kaimin bunkasuwar tattalin arziki.

Zhou ya yi wannan tabbaci ne a wani taron manema labarai a ci gaba da ake yi a babban taron majalisar wakilan jama'ar kasar na shekara shekara.

Gwamnan babban bankin yace a yadda saurin bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin ya ragu, tattalin arzikin kasar ya shiga wani sabon yanayi amma hakan ba ya nufin tattalin arziki kasar na cikin wani yanayi mai matsala ba, haka kuma tsarin kudade na kasar ba zai canza salo ba.

Ma'aunin tattalin arzikin kasar GDP ya na nuna karuwar shi da kashi 7.4 a cikin 100 a bara, adadin da ya fi kankanta tun a shekarar ta 1990, kuma ana sa ran a wannan shekarar ta 2015 zai kai ga kashi 7 ciki 100.( Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China