in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandar kwantar da tarzoma na Sin sun tashi zuwa Liberiya
2015-03-10 20:27:08 cri
A Talatan nan ma'aikatar harkokin tsaron al'umma ta kasar Sin ta sanar da cewa 'yan sandan kwantar da tarzoma na kasar sun tashi zuwa kasar Liberiya domin aiwatar da ayyukan MDD akan tabbatar da zaman lafiya na tsawon watanni 8.

'yan sandan su 140 wadanda suka kunshi mata 5 sun kasance rukuni na uku da kasar Sin ta tura zuwa Liberia dake yammacin Afrika. Kasar Sin ta tura rukunin farko na 'yan sandan kwantar da tarzoman ta da suka hadu da ma'aikatan zaman lafiya na MDD a watan Oktobar 2013.

A yanzu haka akwai 'yan sandan kwantar da tarzoma Sinawa 173 a cikin ayyukan wanzar da zaman lafiya a kasashen da suka hada da Liberiya, Sudan ta kudu, Cyprus da kuma cibiyoyin MDD kamar yadda sanarwar ta bayyana.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China