in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta karfafa dangantakarta tare da Afrika kan masana'antu, kiwon lafiya da tsaro
2015-03-08 16:40:07 cri

Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ya bayyana a ranar yau Lahadi cewa kasar Sin za ta kara karfafa dangantakarta tare da kasashen Afrika a cikin muhimman fannoni uku da suka hada masana'antu, kiwon lafiya da kiyaye tsaro da zaman lafiya.

Za mu karfafa huldarmu tare da nahiyar Afrika, tare da maida hankali kan bukatun nahiyar domin bada kulawa ga wadannan fannoni uku, in ji mista Wang a yayin wani taron manema labarai da aka shirya a lokacin da ake gudanar da babban taron majalisar wakilan jama'ar kasar Sin (NPC).

Faraministan kasar Sin Li Keqiang, a yayin ziyarar aiki da ya kai a nahiyar Afrika a shekarar bara, ya gabatar musammun ma da manyan ayyuka shida da kuma manyan hanyoyi uku na sufuri, wadanda kuma suka samu karbuwa sosai daga kasashen Afrika, in ji ministan. A watan da ya gabata, kasar Sin ta nada darektan farko kan wakilcin dindindin a kungiyar tarayyar Afrika AU, wani matakin da ke nuna a cewar mista Wang, goyon bayan kasar Sin game da dunkulewar Afrika.

Sin da nahiyar Afrika sun jima suna kasancewa cikin makoma guda. A shirye muke mu yi aiki tare da 'yan uwanmu na Afrika da canja dadaddar abokantaka tsakanin Sin da Afrika ta yadda za'a samu alheri da moriya tare, da kuma taimakawa kasashen nahiyar sauya albarkatunsu na cigaba zuwa wani hakikanin karfi na samun bunkasuwa, in ji mista Wang Yi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China