in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar da gwamnan jihar Kano a Najeriya ya kawo nan CRI
2015-03-06 18:14:34 cri

A ranar Talata 2 ga watan Maris ne gwamnan jihar Kano a tarayyar Najeriya Injiniya Rabi'u Musa Kwankwaso ya kawo mana ziyara nan sashen Hausa na gidan rediyon kasar Sin (CRI) a lokacin da ya zo nan kasar Sin don duba daliban jihar ta Kano dake karatu a sassa daban-daban na kasar Sin.

Gwamna Kwankwaso ya bayyana cewa, baya ga sauran kasashen duniya kamar Malaysia, Masar, Poland, Ukraine, Indiya, Ingila da Amurka, akwai kuma kimanin dalibai 25 'yan asalin jihar Kano da ke karatun digiri na biyu da na uku a sassa daban-daban na kasar Sin galibinsu 'ya'yan talakawa.

Yanzu haka, akwai daliban jihar ta Kano sama da dubu biyu da ke karatu a sassa daban-daban na duniya, baya ga wadanda ke karatu a jami'o'i, da sauran manyan makarantun Najeriya.

Injiniya Kwankwaso ya ce, gwamnatin jihar Kano ta gina dakunan kwanan dalibai a jami'o'i daban-daban a tarayyar Najeriya ta yadda wadannan jami'o'i za su rika daukar daliban jihar.

Gwamnan na Kano ya kuma ce, yanzu haka akwai kamfanonin kasar Sin da ke gudanar da ayyukan samar da kayayyakin more rayuwa a jihar kamar gadoji da hanyoyi da ayyukan samar da ruwa da ilimi da sauransu sannan ya tabo kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin Sin da Afirka.

Bugu da kari, ya yi magana a kan siyasar Najeriya da yadda gwamnatinsa ke samar da muhimman kayayyakin more rayuwa da sauran ayyukan da inganta rayuwar al'ummar jihar kano baki daya. (Ibrahim/Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China