in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin zai shugabanci taron muharawa na MDD
2015-02-16 20:20:16 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi zai shugaban ci zaman mahawara na bainin jama'a na kwamitin tsaron MDD a ranar litinin mai zuwa 23 ga wata a matsayin kasar na shugabarda ke shugabantar wannan zagaye na kwamitin a wannan zagaye kamar yadda kakakin ma'aikatar Hua Chunying ta sanar ma manema labarai a nan birnin Beijing.

Ganin kasar Sin ke rike da shugabancin kwamitin na karba karba na wannan watan Fabrairun, ta bada shawarar zaman mahawara na bainin jama'a a litinin mai zuwa karkashin taken kula da zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa don waiwaiye akan tarihi da kuma jaddada muhimmancin da ka'idojin kundin majalissar, inji Madam Hua.

Wannan shekarar ce za'a cika shekaru 70 da kafa majalissar sannan kuma da nasarar kawo karshen yakin duniya na biyu.

Muhawarar zai bada damar da bangarori da dama su waiwayi tarihi su kuma hangi gaban su tare da bayyana ma Duniya duniya shawarar majalaissar na kare zaman duniya da tsaro.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China