in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabon Sarkin Saudiyya zai cigaba da bin maunfofin da ya kuma bayyana sabbin mukamai
2015-01-23 20:55:28 cri
A yau jumma'a bayan darewar karagar Sarauta bayan rasuwar Sarkin Abdallah bin Abdul-Aziz a daren jiya, sabon Sarkin Saudi Arabia Salman bIn Abdul-Aziz al Saud ya ce zai cigaba da bin tsarin da tsohon Sarki ya fitar na mulki.

Sarki Salman bIn Abdul-Aziz al Saud ya bayyana hakan ne ta jawabinsa ta kafar yada labaran kasar da suka hada da Talabijin, tare da sanar da zaman makoki bisa ga rasuwar tsohon Sarkin da ya yi Sarauta kusan shekaru 20.

A jawabinsa Sarki Salman ya ambaci halin rudanin da ake ciki a yankin gabas ta tsakiya saboda yaduwar kungiyar mayakan IS, inda yace Larabawa da kasashen Musulmai suna matukar bukatar hadin kai da goyon baya.

Haka kuma, Sarki Salman ya mika ta'aziyar sa ga daukacin al'ummar kasar, da larabawa da ma Musulman duniya baki daya sannan ya jinjina ma Marigayi Sarki Abdallah bisa ga kokarin shi a yankin da sauran kasashen duniya baki daya.

A daga bisani kuma Sarki Salman ya sanar da sabon Yarima mai jiran gado da wassu sabbin mukaman gwamnatin.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China