in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta mika wani babban jirgin ruwa ga Nigeriya
2014-11-27 20:43:06 cri
Kasar Sin ta mika wani babban jirgin ruwan tsaron teku ga gwamnatin Nigeriya a ranar Alhamis din nan.

Jirgin da kamfanin kera jiragen ruwa na CSIC wato China Shipbuilding Industry Corporation an mika shi ne ga kasar Nigeriya a birnin Qidong, dake lardin Jiangsu na gabashim kasar Sin.

Jirgin mai tsawon mita 95.5 da fadin mita 12.2 yana iya fitar da ruwa da ya kai tan 1,800, abinda ya sa zai zama mafi girma kuma mai dauke da kayan zamani cikin jiragen ruwan tsaron teku da Nigeriya ke da su a yanzu,in ji kamfanin na CSIC.

Wannan jirgin za'a yi aiki da shi wajen tabbatar da tsaro akan tekun kasar, sa ido da lura da rijiyoyin man da kasar ke da su, sannan kuma za'a yi amfani da shi wajen ayyukan da ya shafi kamun kifi, bada ceto da dai sauran su.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China