in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana sa ran taron G20 dake tafe zai samu nasara a bangarori 4
2014-11-13 20:45:08 cri
Kasar Sin tana sa ran a lokacin taron G20 dake tafe za a samu sakamako babba a bangaren bunkasa tattalin arziki, inganta sha'anin mulki, raguwar kangiya a bangaren cinikayya, da kuma daidaita kalubalolin duniya.

Kamar yadda shugaban sashin tattalin arziki na kasa da kasa a ma'aikatar harkokin wajen kasar Zhang Jun ya shaida ma manema labarai a alhamis din nan, ya ce shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci taron karo na 9 na shugabannin kungiyar G20 da za'a yi a birnin Brisbane na kasar Australiya. tsakanin ranakun 15 zuwa 16 ga watan nan na Nuwamba.

Mr. Zhang ya kara da cewa a lokacin taron shugaba Xi zai yi bayanin matsayar kasar game da manyan batutuwan da suka shafi tattalin arzikin duniya, zai kuma bada shawarwari, da tayin kara hadin gwiwa a wannan taron.

Xi Jinping zai yi aiki tare da sauran mambobin kungiyar domin samar da hanyar samar da cigaba, inganta rayuwar jama'a da kuma kara azama ga tafiyar da harkokin tattalin arzikin duniya.

A wani bangaren na taron G20 kuma, shugaba Xi Jinping zai halarci taron kasashen BRICS wato kasashen Brazil,Rasha,India,Sin, da kuma Afrika ta kudu.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China