Shugaba Xi yace za su hada karfi waje daya domin taimakawa kasashen Afrika su kara samun damar magance tare da shawo kan wannan annoba.
Kungiyar ta APEC tana mara wa MDD baya a kokarinta na agaza ma Afrika shawo kan wannan annoba, Shugaban na Sin yana bayanin hakan ne a taron manema labarai bayan kammala taron karo na 22 da aka yi a dakin taro na tabkin Yanqi dake arewacin birnin na Beijing. (Fatimah)