Shugaba Obama ya bayyana hakan ne yau Litinin a nan birnin Beijing yayin da ya ke jawabi a taron kolin kungiyar APEC na wannan shekara da ke gudana a nan kasar Sin.
Ya ce, alfanun hadin gwiwar kasashen biyu, ba kawai ta tsaya ga kasashen ne kawai ba har da duniya baki daya.
Don haka ya ce, kasancewarsu manyan kasashen duniya biyu, kasashen suna da wani nauyi na musamman da ya rataya a wuyansu, kuma idan kasashen biyu suka yi aiki tare babu shakka duniya za ta amfana matuka.
Ya ce, ci gaban da kasar Sin ta samu a harkokin tattalin azriki ya dace da muradun Amurka da ma duniya baki daya.(Ibrahim)