in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kira taron yaki da zuba jarin tallafawa harkokin ta'addanci a Bahrain
2014-11-10 17:22:04 cri
A jiya Lahadi ne aka gudanar da taron kasa da kasa na yini guda kan yaki da zuba kudin tallafawa harkokin ta'addanci a kasar Bahrain, inda mahalarta taron daga kasa da kasa suka tattauna kan harkar hana kungiyoyin 'yan ta'adda samun kudin shiga.

Ministan harkokin waje na kasar ta Bahrain Khaled al-Khalifa a jawabin da ya gabatar ya ce, kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta IS tana samun kudade ne ta hanyar wawushe bankuna da kuma mallakar rijiyoyin mai a sassan da ta mamaye. Ban da haka, wasu mutane masu zaman kansu da kuma kungiyoyi ma suna tallafawa kungiyar ta IS da kudade. Don haka, ministan ya yi kira ga kasa da kasa da su kafa wani tsari na tabbatar da cewa, an toshe dukkan kafofin shigowar kudi da ke shigowa hannun kungiyoyin 'yan ta'adda, tare kuma da hana kungiyoyin 'yan ta'adda gudanar da haramtattun harkokin ciniki da suka hada da fasa kwauri.

Wakilai daga kasashen Amurka, Birtaniya, Faransa, Rasha, Sin da kuma kasashen Larabawa da ma bankin duniya da asusun ba da lamuni na duniya sun halarci taron da aka yi a wannan rana.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China