in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU da MDD sun tattauna game da yanayin da ake ciki a yankunan Great Lakes
2014-11-10 17:14:26 cri
Kungiyar tarayyar Afirka AU da MDD sun tattauna game da halin da ake ciki a yankunan nan na Great Lakes, a kokarin da ake na ganin an aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da tsaro a jamhuriyar demokuradiyar Congo(DRC) da kuma yankin baki daya.

Wata sanarwar da kungiyar AU ta bayar ta ce, kwamishinan kula a harkokin zaman lafiya da tsaro na kungiyar AU Smail Chergui da manzon musamman na babban sakataren MDD mai kula da yankin Great Lakes Said Djinnit sun gana a ranar Lahadi a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha kan wannan batu.

Sanarwar ta ce, ganawar ta ba su damar nazarin yadda za a aiwatar da yarjejeniyar da kuma manufar kokarin da ake na tabbatar da zaman lafiya,tsaro,kwanciyar hankali da ci gaba a yankunan na Great Lakes.

Bugu da kari, tattaunawar ta mayar da hankali kan shirye-shiryen taro na gaba da aka shirya gudanarwa a watan Janairun shekarar 2015 a Addis Ababa, yayin taron kolin kungiyar ta AU.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China