in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na fatan bunkasa sabuwar dangantaka da Amurka
2014-11-05 20:22:28 cri
Kasar Sin ta kara jaddada kudurinta na yin aiki tare da kasar Amurka wajen gina sabuwar dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu, duk da irin bambance-bambancen da ke tsakaninsu.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ne ya bayyana hakan yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai game da jawabin da sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry ya yi yayin wata lacca a birnin Washington, inda ya bayyana muhimmancin karfafa dangantaka tsakanin Amurka da Sin.

Hong Lei ya ce, idan sassan biyu suka yi hadin gwiwa yadda ya kamata a matakan shiyya-shiyya da duniya baki daya, hakan zai taiamaka wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Asiya da Fasifik da ma duniya baki daya.

Kasar Sin na fatan yin aiki tare da Amurka wajen hanzarta aiwatar da yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen biyu suka cimma ta yadda za a gina sabuwar dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu ba za su tsokani juna ba, mutunta juna da samun moriya tare don amfanin al'ummomin kasashen biyu da ma duniya baki daya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China