in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar sin ta yi kira da a samu zaman lafiya a Burkina Faso
2014-11-04 20:35:42 cri
Kasar Sin ta yi kira ga dukkan bangarori a kasar Burkina Faso da su warware bambance-bambance da ke tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari don dawo da doka da oda a kasar, sakamakon boren da ya yi awon gaba da shugaban kasar.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying wadda ta bayyana hakan yau yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa ta ce, kasar Sin na sa ido kan halin da ake ciki a kasar ta Burkina Faso.

Ta ce, kasar Sin na fatan dukkan bangarorin da batun ya shafa za su yi la'akari da muradun kasar da al'ummarta kana su warware dukkan bambance-bambance da ke tsakaninsu ta hanyar hawan teburin sulhu da tuntubar juna don ganin an maido da zaman lafiya da ci gaba a kasar.

Madam Hua ta bayyana cewa, har kullum kasar Sin daya tak a duniya na martaba manufofi biyar na kasancewa cikin zaman lafiya ta yadda za ta bunkasa dangankatar abokantaka da sauran kasashe. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China