in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matakan da kasashen duniya suke dauka kan Ebola
2014-10-29 08:46:57 cri

Tun lokacin da aka fara gano cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo a shekarar 1976, cutar ta ci gaba da yaduwa a tsakanin kasashen gabashin Afirka, sannan ta bullo a kasar Guinea a watan Fabrairu inda take ci gaba da yaduwa a sassan kasar.

Yanzu haka cutar Ebola ta halaka mutane sama da 4,000 tun bayan da cutar ta bullo a kasashen yammacin Afirka da suka hada da Liberia, Guinea, Saliyo da kuma wasu kalilan a Najeriya baya ga wasu sama da dubu 8 da suka kamu da cutar. Wannan ya sa wasu kasashen da ke makwabtaka da wadannan kasashe da ke fama da wannan cuta daukar wasu matakai da suka hada da rufe kan iyakokinsu, dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa kasashen ko daukar fasinjojin da suka fito daga wadannan kasashe.

Baya ga kasashen yammacin Afirka da ke fama da wannan cuta, yanzu haka an samu rahoton mutuwar masu dauke da cutar a kasashe kamar Amurka, Jamus da wasu kasashen Turai. Wannan ya sa kasashe irin su Amurka da Burtaniya daukar matakan binciken zafin jikin fasinjojin da suka shigo kasar ta jiragen sama daga kasashen da ke fama da wannan cuta don hana yaduwar cutar a cikin kasashen su.

Hukumar lafiya ta duniya WHO da wasu kasashe, ciki har da kasar Sin sun aike da taimakon kayayyakin kiwon lafiya da tawagar ma'aikatan lafiya zuwa kasashen da suke fama da wannan cuta.

Har yanzu cutar Ebola mai saurin kisa ba ta da magani, don haka ma'aikatan lafiya ke kira ga jama'a da su kara daukar matakan kariya daga kamuwa da cutar, yayin da gwamnatocin kasashen da ke fama da cutar ke kara fadakar da jama'a tare da ware makuden kudade don tunkarar wannan cuta da yanzu haka ta kasance mafi hadari a duniya. (Ibrahim/Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China