in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya yi kira da kada a tsoma baki a cikin harkokin cikin kasar
2014-10-02 17:02:50 cri
Ministan harkokin kasashen wajen kasar Wang Yi a ranar laraban nan yace harkokin da ya shafi yankin Hong Kong harkoki ne na cikin gida na kasar Sin don haka ya zama wajibi kasashen waje su guji tsoma baki a cikin abin da ya shafi 'yan cin kasar.

Ministan ya jaddada matsayin gwamnatin kasar Sin ne game da abin da ke faruwa a yankin Hong Kong lokacin da ya gana da Shugabannin kasar Amurka a fadar White house da kuma ma'aikatar harkokin kasar inda yace wannan ka'ida ce da ta shafi huldar da ke tsakanin kasa da kasa.

Boren mai taken mallakan tsakiyar an fara shi ne a safiyar ranar lahadin data gabata a cibiyar gwamnatin yankin dake Admiralty a cikin garin na Hongkong daga baya kuma aka samu karuwan masu zanga zanga a tsakiyar birnin da unguwannin causeway bay da Mongkok abin da ya kawo cunkoson ababen hawa da rufe makarantu.

A game da hakan Mr.Wang yace yana da imanin cewa kowane kasa kowane al'umma ba wanda zai amince da wannan ayyukan rashin da'a wanda ya lalata zaman rayuwar al'umma.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China