
140922-Hajiya-Halimatu-Said-I-Kande.m4a
|
A yau shirin "In Ba Ku Ba Gida" yana farin cikin gabatar muku wata babbar bakuwa mai suna Halimatu Sa'id. Wadda baiwar Allah ce mai fafutukar yada addinin Musulunci a Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya. Malama Halimatu ta bude makarantun allo guda 7 domin koyar wa yara ka'idojin addinin musulunci.

A zantawarta da wakilinmu Murtala, Hajiya Halimatu ta yi mana bayani kan tarihin rayuwar ta, da kuma yadda ta kafa wadannan makarantun allo bakwai. Sa'an nan ta yi mana karin haske kan dalilin da ya sa ta himmar kwazo wajen kare hakkin mata.(Kande Gao)
