in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya bukaci a inganta hadin gwiwa tsakanin kasar sa da kungiyar EU
2014-09-07 16:16:20 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana bukatar dake akwai, ta kara inganta hadin gwiwar dake tsakanin jama'ar kasarsa da ta kasashe membobin kungiyar tarayyar Turai ta EU.

Shugaba Xi wanda ya bayyana hakan cikin wata wasikar da ya aike ga babban taron tattaunawa na wakilan bangarorin biyu da ya gudana jiya Asabar a nan birnin Beijing, ya ce ya dace bangarorin 2 su dukufa wajen musayar ra'ayoyi game da batutuwan da ke iya bunkasa rayuwar jama'un su, musamman a fannonin ilmi da kimiyya, al'adu, da yada labaru. Sauran fannonin sun hada da na inganta rayuwar matasa da mata, bangarorin da a cewar shugaban kasar ta Sin su ne ginshikan habaka dangantakar EU da kasar ta Sin.

A daya bangaren kuma shugaba Xi ya bayyana alakar dake tsakanin kasarsa da EU a matsayin daya daga cikin manyan huldodin ci gaba a duk fadin duniya, yana mai cewa taruka irin wadannan za su taimaka matuka wajen habaka ci gaban sassan biyu, wajen samar da dauwamammen yanayin zaman lafiya da ci gaba, da damar gudanar da gyare- gyare tare da wayewar kai.

Manyan baki a wajen taron na wannan karo dai sun hada jagororinsa, wato mataimakiyar firaministan kasar Sin Liu Yandong, da kuma kwamishinan sashen Ilimi, al'adu yaruka da inganata rayuwar matasa na EU Androulla Vassiliuo. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China