in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin cikon shekaru 87 da kafa rundunar sojojin jama'ar kasar Sin a ofishin jakadan kasar dake Najeriya
2014-08-01 20:09:47 cri
A jiya Alhamis 31 ga watan Yuli ne, aka shirya wata liyafa a ofishin jakadan kasar Sin dake Najeriya a Abuja, babban birnin tarayyar kasar, domin murnar cikon shekaru 87 da kafa rundunar sojojin jama'ar kasar Sin.

A jawabin da ya yi, jami'in sojan bangaren Sin janar Kang Honglin ya bayyana cewa, an samu cikakkiyar nasara a ziyarar aiki da firaministan kasar Sin Li Keqiang ya kawo Najeriya a watan Mayu na bana.

A yayin ziyarar, gwamnatocin kasashen biyu sun cimma ra'ayi daya kan hadin gwiwarsu ta fuskokin zaman lafiya da tsaron kasa.

A nasa bangaren, wakilin musamman na hafsan-hafsoshin sojojin ruwan Najeriya, kuma shugaban sashen tsare-tsare na hedkwatar rundunar sojan ruwan kasar manjon janar Izzi Oda a yayin jawabinsa ya nuna yabo ga nasarorin da rundunonin soja na kasashen biyu suka samu a shekara daya da ta wuce, ya kuma yi godiya ga kokarin da bangaren Sin ya yi na inganta bunkasuwar dangantakar dake tsakaninsu, yana mai fatan za a kara zurfafa da daga matsayin hadin kai a tsakaninsu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China