Shugaban majalissar dattawan tarayyar Najeriya David Mark, ya yi kira ga kungiyar kwallon kafar kasar ta Super Eagles, da ta zage damtse wajen ganin ta doke kasar Faransa a wasan da za su buga a Litinin din nan.
Mr. Mark wanda tun da farko, ya jagoranci tawagar gwamnatin kasar zuwa bikin bude gasar cin kofin duniyar da ake ci gaba da bugawa yanzu haka a kasar Brazil, ya bukaci 'yan wasan Najeriyar da su sanya kwazo da himma a wasan su na gaba, kamar yadda suka faro a baya.
Shugaban majalissar dattawan tarayyar Najeriyar ya kara da cewa, nasarar Super Eagles, nasara ce ga nahiyar Afirka baki daya. Daga nan sai ya jaddada alkawarin gwamnatin tarayyar Najeriyar, na baiwa kungiyar dukkanin tallafi da kwarin gwiwa, da kuma tukuicin da aka alkawarta musu. (Saminu)