in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Afghanistan
2014-05-19 20:37:19 cri
A yau Litinin ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Afghanistan Hamid Karzai a birnin Shanghai na kasar Sin, inda ya lashi takwabin taimakawa kokarin kasar na tabbatar da cikakken 'yanci da yankunanta.

Shugaba Xi ya ce kasar Sin sahihiyar abokiyar kasar Afghanistan ce duk da irin canje-canjen da ake fuskanta a harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya. Don haka ya lashi takwabin hada kai da kasar Afghanistan don daukar matakan da suka dace na gina hanyar siliki na tattalin arziki, kuma kasar Sin na goyon bayan kamfanoninta da su zuba jari a Afghanistan.

A nasa bangaren Shugaba Karzai ya yaba da dangantakar abokantaka da ke tsakanin kasashen biyu, inda ya ce kasar Sin sahihiyar makwabciya ce. Afghanistnan ta yaba da irin goyon bayan da take bayar wa wajen sake gina kasar cikin lumana.

Shugaba Karzai ya zo Sin ne don halartar taron kolin tattaunawa kan inganta cudanya da karfafa hadin gwiwa a nahiyar Asiya da aka shirya gudanarwa a ranar Talata da Laraba a birnin Shanghai. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China