in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin zai kai ziyara ga kasashen Habasha, Najeriya, Angola, Kenya da hedkwatar AU
2014-04-30 12:45:33 cri
A yau Laraba 30 ga wata ne, Mr. Qing Gang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya sanar da cewa, bisa gayyatar da takwaransa na kasar Habasha Hailemariam Desalegn, shugaban kasar Najeria Goodluck Ebele Jonathan, shugaban kasar Angola Jose Eduardo dos Santos and shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta suka yi masa, Li Keqiang, firayin ministan kasar Sin, zai kai ziyarar aiki a wadannan kasashe hudu tun daga ran 4 zuwa ran 11 ga watan Mayu.

Sannan bisa gayyatar da Mohamed Ould Abdel Aziz, shugaban wannan zagaye na kungiyar kawancen kasashen Afirka AU, kuma shugaban kasar Mauritania da shugabar hukumar zartaswar kungiyar AU Nkosazana Dlamini-Zuma suka yi masa, Mr. Li zai kuma kai ziyara hedkwatar AU dake birnin Addis Ababa a ran 5 ga watan Mayu.

Bugu da kari, bisa gayyatar da shugaba Klaus Schwab na dandanlin tattaunawar tattalin arzikin kasa da kasa ya yi masa, Li Keqiang zai halarci cikakken zama na dandanlin tattalin arzikin kasa da kasa kan Afirka da za a yi a birnin Abuja na Najeriya a ran 8 ga watan Mayu. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China