in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Goodluck Jonathan ya nada shugabannin taron kasa
2014-03-04 16:26:14 cri

Yayin da babban taron tattauna makomar kasa ke kara kusantowa a Najeriya, shugaba Goodluck Jonathan ya amince da nada mutane uku, da zasu jagoranci gudanar da taron.

Shugabannin da za su jagoranci taron, kamar yadda sakataren gwamnatin tarayya, Anyim Pius Anyim ya bayyana cikin wata sanarwa, ya ce su ne tsohon babban mai shari'a Dr. Idris Kutigi a matsayin shugaba, sai tsohon ministan harkokin cikin gida, Bolaji Akinyemi a matsayin mataimakin shugaba, yayin da kuma Dr. Valerie Azinge za ta kasance a matsayin sakatariya.

Kamar yadda sanarwar ta bayyana, shugaban da sauran mataimakansa, za su kama aiki ne a ranar Larabar nan 5 ga watan Maris.

Sauran wakilai 492 da za su wakilci jama'ar kasar kuwa, za'a rantsar da su don fara ayyukansu a ranar 10 ga watan nan, kamar dai yadda shugaba Jonathan ya bayyana yayin tattaunawar da yayi kai-tsaye da manema labaran kasar a kwanan baya.

Murtala, wakilin sashin Hausa na CRI, daga Abuja, Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China