in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dole ne a raya kasashen Afrika ta hanyar bunkasa masana'antu, in ji shugaban kasar Najeriya
2014-02-25 14:40:20 cri
A jiya Litinin 24 ga watan nan ne kafofin watsa labaru a tarayyar Najeriya, suka ruwaito shugaban kasar Goodluck Jonathan, na cewa wajibi ne a bunkasa masana'antun kasashen dake nahiyar Afrika, muddin ana fatan fidda nahiyar daga mawuyacin halin da take ciki.

Shugaba Jonathan wanda ya bayyana hakan yayin wani bikin kaddamar da kwamitin kula da harkokin bincike da kirkire-kirkire na kasar a kwanan baya, ya kara da cewa kwalliya ba zata biya kudin sabulu ba, muddin kasashen Afrika suka ci gaba da dogaro kan kananan kayan da ake sarrafawa, da kuma danyun kaya wajen neman bunkasuwa.

Yace kamata yayi a zabi wata hanyar raya masana'antu da za ta inganta hada hadar kayayyakin cinikayya, da kuma samar da guraban aikin yi. Jonathan ya ce dole ne a canza yanayin da ake ciki a Najreiya, da ma nahiyar ta Afrika baki daya.

Sabon kwamitin da aka kafa dai zai kasance jigon tsara manufofin kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha a kasar, wanda kuma shugaban kasar zai jagoranta, baya ga wasu ministocin kasar da zasu kasance mambobin sa. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China