in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane fiye da dubu 400 sun yi asara sakamakon girgizar kasa a jihar Xinjiang
2014-02-16 17:37:06 cri
Hukumar dake kula da harkokin yankin He Tian na jihar Xinjiang na Uighur mai cin gashin kanta ta kasar Sin ta kira wani taron a yammacin ranar asabar 15 ga wata kan girgizar kasa da ya auku a gundumar Yu Tian mai maki 7.3, inda aka ba da rahoton cewa, mutane da suka kai 455,573 sun yi asara a cikin bala'in, yayin da wasu gidaje 236,808 suka lalace.

Ya zuwa karfe 6 na dare a ran 14 ga watan Fabrairu, babu rahoton samun hasarar rayuka ko jikkatan jama'a, amma bala'in ya yi sanadiyyar lalacewar gidaje da dama, tare kuma da kashe dabbobi masu yawa, wassu gadoji sun fada, abin da ya kawo babbar asarar dukiya ga yankin He Tian.

Wani babban jami'in yankin He Tian ya bayyana a wannan rana cewa, bayan aukuwar bala'in, hukumar harkokin cikin gida na jihar ta dauki matakin tinkarar bala'i da ya dace cikin lokaci, tare kuma da samar da wasu kayayyakin tallafi cikin gaggawa, gami da tsugunar da wadanda wannan bala'in ya shafa su 85,676. Ya zuwa yanzu, an samu isashen tantuna, bargunan rufa, shinkafa da dai sauran kayayyakin yau da kullum, ban da haka, ana tafiyar da harkokin zirga-zirga, sadarwa, wutar lantarki, ruwan sha yadda ya kamata. An ba da labari cewa, jama'ar wurin sun samu kwanciyar hankali, al'umma na cikin natsuwa sannan ana zama rayuwa yadda ya kamata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China