in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Kenya ta amince da kafa yankin ciniki mai yanci na farko a kasar
2014-02-14 12:35:43 cri
A ranar 13 ga watan nan ne gwamnatin kasar Kenya ta zartas da kudurin kafa yankin ciniki mai 'yanci na farko a birnin Mombasa da ke gabashin kasar.

Sanarwar da gwamnatin Kenya ta bayar a wannan rana ta nuna cewa, kafa wannan yankin ciniki mai 'yanci zai taimaka ga inganta harkokin ciniki a tsakanin sassan gabashin Afirka da na tsakiyar Afirka da kuma na kudancin nahiyar. Har ila yau, 'yan kasuwa da ke kasar da sauran sassan shiyyar za su iya sayen kayayyakin da suka ga dama a wannan yankin ba tare da zuwa kasashen hadaddiyar daular larabawa da Sin ko Japan da a baya suka saba ba.

An ce, gwamnatin Kenya ta kebe filin da fadinsa ya kai muraba'in kilomita 3400 domin kafa yankin, wanda ya hada da muraba'in kilomita 2000 da ke Mombasa.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China