Bayan aukuwar bala'in, shugaban kasar Sin Xi Jinping da firaministan kasar Li Keqiang sun ba da umurni ga hukumomi da abin ya shafa na wurin da su ba da kulawa ga wuraren dake fama da bala'in da ba da jiyya da aikin ceto cikin gaggawa, tare kuma da sa ido kan bala'in ta yadda za a ba da tabbaci da kare dukiyar jama'a a wurin. An ce ya zuwa karfi 6 da mintoci 30 na yamma, hukumar rage radadin bala'in, ma'aikatar harkokin cikin gida sun mai da martani cikin loakci kan bala'in tare kuma da tura rukunonin ma'aikata zuwa wurin domin taimakawa jihar wajen yaki da bala'in da tsugunar da wadanda suke fama da matsala. (Amina)