in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban magatakardar MDD zai halarci bikin bude wasannin Olympic a Rasha
2014-02-04 16:49:30 cri
Rahotanni daga helkwatar MDD sun bayyana cewa babban magatakardan majalissar Ban Ki-Moon, zai halarci bikin bude wasannin Olympic na lokacin sanya na bana a garin Sochi na kasar Rasha.

A cewar kakakin majalissar Mertin Nesirky, Mr. Ban zai yi amfani da wannan dama wajen ganawa da sauran shugabanni da za su halarci bikin wanda za a gudanar a ranar Juma'a 7 ga watan nan na Fabarairu a birnin Sochin kasar ta Rasha.

Haka zalika bikin na bana zai baiwa Mr. Ban damar gabatar da jawabi ga mambobin babban kwamitin shirya wasannin Olympic na kasa da kasa wato IOC.

Nesirky ya kara da cewa alakar dake tsakanin MDD da kwamitin IOC na samun tagomashi, wanda hakan na daya daga manyan dalilan da suka sanya babban magatakardan majalissar bayyana aniyyarsa ta halartar wannan biki.

Ana dai sa ran gudanar da gasannin Olympic din na bana ne tsakanin 7 zuwa 23 ga watan nan da muke ciki. Sa'an nan wasannin Olympic na ajin nakasassu karo na 11 ya biyo baya, daga 7 zuwa 16 ga watan Maris dake tafe, duka dai a birnin na Sochi. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China