in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yaba ma ayyukan Sin wajen samar da ababen more rayuwa don cigaban Afrika.
2014-01-29 10:20:28 cri
Kasar Sin tana aiwatar da ayyukan cigaban Afrika wadanda suka zama abin a yaba, in ji Elham Mahmoud Ibrahim, Kwamishinar kula da ababen more rayuwa da makamashi na kungiyar tarayyara kasashen Afrika AU.

Kwamishinar ta lura cewa, kasar Sin tana ayyukan a zo a gani na cigaba da suka hada da shimfida hanyoyin mota da layin dogo, gadoji filin saukar jiragen sama, filin wassannin motsa jki a cikin sauran ayyukan da take yi.

Elham Mahmoud Ibrahim ta ce, yadda Sin take gudanar da manyan ayyukan ta a kasashen Afrika, haka take aiwatarwa a yankuna da shiyya shiyya wadanda suka taimaka kwarai wajen ayyukan samar da ababen more rayuwa a nahiyar, wato PIDA.

A cewar Kwamishinar, zuba jari na daya daga cikin kalubale na kayayyakin cigaba a Afrika. Ya ce kalubalen su ne ababen more rayuwa ba su isa ba kuma ba su da inganci. Don haka akwai bukatar a zuba jari sosai. (Fatimah Jibri)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China