in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta taya sabon shugaban kasar Madagaskar murna
2014-01-20 20:54:04 cri
Kasar Sin ta bakin kakakin ma'aikatar harkokin wajenta, Hong Lei a Litinin din nan 20 ga wata, ta taya sabon Shugaban kasar Madagascar Hery Rajaonarimapianina murna bisa ga mukaminsa.

Mr Hong ya sanar da hakan ne a ganawar da ya yi da manema labarai wanda aka saba yi duk rana a nan birnin Beijing, fadar gwamnatin kasar, lokacin da aka bukaci ya yi bayani game da sahihancin zaben shugaban kasar ta Madagascar.

Kotu ta musamman game da zaben Shugaban kasar ta Madagascar a ranar Jumma'ar da ta gabata ne ta sanar da sunan Hery Rajaonarimampianina a matsayin wanda ya lashen babban zaben shugaban kasar a zagaye na biyu da aka yi a ranar 20 ga watan Disambar bara da kashi 53.49 a cikin 100 abin da ya nuna ya doke abokin hamayyarsa Jean Louis Robinson.

Mr Hong ya ce kasar Sin tana fatan Madagascar za ta kawo karshen rikicin siyasarta sakamakon wannan zabe, sannan ta samu daidaituwar kasar da ci gaba mai dorewa. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China