in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundanar sojojin Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutane a wani harin da aka kai a jihar Borno
2014-01-15 12:27:50 cri

Hukumomin tsaron kasar Najeriya sun tabbatar a ranar Talata cewa, mutane da dama suka mutu yayin da wasu suka jikkata a cikin wani harin kunar bakin wake a wani yankin kasuwanci dake Maiduguri, hedkwatar jihar Borno. Nakiyoyin sun fashe a gaban tashar binciken jami'an tsaro da ake kira FOI dake bangare na hudu a tsakiyar birnin da misalin karfe biyu na rana, agogon wurin. Mohammed Dole, kakakin rundanar sojoji ta 7, ya bayyana cewa, ana zargin mambobin kungiyar Boko Haram da kai harin.

A cikin wata sanarwa da aka aika wa kamfanin dillancin labarai na Xinhua, kakakin bai ba da adadin yawan mutanen da suka mutu ba, amma wasu da lamarin ya abku gaban idonsu sun ce, mutane sama da goma sun mutu.

Sai dai mista Dole ya ce, an kama wani mutumin da ake zargi, kuma tuni manjo janar Junaid Bindawa, babban ofisa na rundunar sojojin jihar ya ba da umurnin gudanar da bincike mai zurfi kan wannan lamarin.

Harin dai ya abku lokacin ranar hutu ta kasa domin tunawa da haifuwar manzon Allah, kuma muhimmin lokaci ne da mutane suke gudanar da harkokin kasuwanci sosai.

Jihar Borno na fama da hare-haren kungiyar Boko Haram tun daga shekarar 2009, a lokacin da kungiyar ta fara kai hare-harenta kan gine-ginen kristoci, gine-ginen jami'an tsaro, makarantu da kauyuka. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China