in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya nuna damuwa kan tashin hankalin da ke karuwa a yankunan Isra'ila da Palasdinu
2013-12-25 15:15:43 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon, ya bayyana damuwa matuka game da barkewar tashin hankali a yankunan Isra'ila,Gaza da yammacin kogin Jordan,bayan da Isra'ila ta kai wasu hare-hare ta sama kan zirin Gaza,inda suka kashe wata yarinya tare da jikkata wasu fafaren hula.

Mr Ban ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya bayar ta hannun kakakinsa,inda ya yi allahwadai da kisan na Gaza da kuma bam din da aka dana cikin wata motar Bas a kusa da birnin Tel Aviv ranar Lahadi.

Babban sakataren na MDD ya kuma yi amfani da wannan dama wajen mika ta'aziyarsa ga iyalan wadanda hare-haren suka shafa. Kafofin watsa labarai na bayyana cewa,hare-haren sun zo ne bayan da wasu maharan Palasdinawa suka harbe wasu 'yan Isra'ila har lahira yayin da suke kokarin gyara shingen tsaro.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China