in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gyara dokar kararraki da suka shafi gudanar da mulki a kasar Sin
2013-12-24 16:57:27 cri
A 'yan kwanakin baya ne aka yiwa dokar gabatar da kararraki da suka shafi gudanar da harkokin mulki a nan kasar Sin gyaran fuska, matakin da ya kasance karo na farko cikin shekaru 20 da suka gabata. Don gane da hakan a ran 23 ga watan nan an gabatar da daftarin dokar ga babban sashen lura da kafa dokoki don nazartar daftarin.

Cikin wannan daftarin dokar an mai da hankali kan karfafa ikon jama'a, da wasu kungiyoyin kasa wajen daukaka kara, da nufin kiyaye hakkokin al'umma ta hanyar dokoki yadda ya kamata.

Don gane da hakan, wasu masana na ganin cewa an gyara dokar ne don karfafa aikin sa ido kan hukumomi masu alaka da gudanar da mulkin kasa, ta hanyar yin amfani da wannan doka ta gabatar da kararraki. Haka zalika daftarin ya tanaji karfafa hanyoyin kiyaye hakkin jama'a, da wasu kungiyoyin kasa yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China