in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Larabawa sun bukaci Saudiyya da ta janye matakin da ta dauka na kin zama a kwamitin tsaro na MDD
2013-10-20 16:19:37 cri
Gungun kasashen Larabawa dake cikin kungiyar MDD sun kira a ranar Asabar, 19 ga wata ga kasar Saudiyya da ta yi kokarin janye matakin da ta dauka na kin zama mamban da aka zaba a kwamitin tsaro na MDD.

Hukumomin Riyadh sun bata wa gamayyar kasa da kasa da rai a lokacin da suka bayyana kauracewarsu daga kwamitin tsaro na wa'adin shekaru biyu, kujerar da kasar ta yi takarar nema kuma aka zabe ta a ranar Alhamis a yayin babban taron na MDD.

Shugabannin Saudiyya ya kamata su amince da zamansu a kwamitin tsaro da kuma ci gaba da ba da kokarinsu na bajinta wajen kare bukatunmu, musamman ma a dandalin kwamitin sulhu, in ji gungun wadannan kasashen Larabawa a cikin wata sanarwa.

Wakilan kasashen Larabawa sun bayyana girmamawa da nuna fahimtarsu kan matakin da Saudiya ta dauka dake bayyana matsayin gamayyar kasashen Larabawa da kuma al'ummar musulmi a wannan muhimmin lokaci da tarihi, musamman ma shiyyar yankin Gabas ta Tsakiya, in ji wannan sanarwa.

A ranar Jumma'a ne dai ministan harkokin wajen kasar Saudiyya ya bayyana matakin na kauracewa zama a kwamitin tsaro na MDD har sai an yi wa kwamitin gyaran fasali ta yadda zai cika aikinsa da nauyin dake bisa wuyansa na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China