Gobe Talata 15 ga watan Oktoba, rana ce da jama'ar Musulmi dake Najeriya da Nijar da kuma sauran wasu kasashen duniya za su yi bikin babbar sallah. Kwanan baya, wakilinmu Murtala dake Najeriya ya yi tattaki zuwa babban masallacin dake birnin Abuja, tarayyar Najeriya, wato Central Mosque, inda ya yi hira da mataimakin babban limamim masallacin malam Muhammed Kabir Adam dangane da babbar salla, don fadakar da jama'a masu sauraro. Yanzu ga cikakken rahoton da Murtala ya aiko mana.