in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar gamayyar 'yan adawar Siriya za su zabi Firaministan rikon kwarya
2013-09-14 16:50:48 cri
Kungiyar gamayyar 'yan adawar kasar Siriya dake ketare ko SNC a takaice, ta kira babban taronta a birnin Santanbul na kasar Turkiyya a ranar Jumma'a 13 ga watan nan, domin gudanar da zaben Firmainstan ta na rikon kwarya.

Rahotanni dai na bayyana cewa, yayin zaman sirri da mambobin majalissarta su 155 suka yi a jiya Jumma'a, an bayyana sunan Ahmad Tumeh al-Khader, a matsayin dan takarar mukamin mafi dacewa. Baya ga batun zaben Firamanistan rikon kwarya, ana sa ran SNC za ta bayyana matsayarta don gane da shawarar da shugaban kasar Rasha ya gabatar game da kasar Siriya.

Yayin wani taron 'yan jarida da ya gudanar, jagoran sashen yada labaran kungiyar ta SNC Khalid Saleh, ya bayyana cewa gamayyar kungiyar ta 'yan adawa na da matukar burin ganin kasashen duniya sun amince da shawarar hukunta wadanda ke da hannu, cikin hare-hare da makamai masu guba da aka kai kan fafaren hula a kasar ta Siriya. Har ila yau Saleh, ya jaddada bukatar samun karin kudaden tallafi ga 'yan adawar daga kasahen ketare. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China