in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Mugabe na Zimbabwe ya yi rantsuwar kama aiki
2013-08-22 20:13:50 cri
A yau Alhamis ne aka rantsar da Robert Mugabe mai shekaru 89 a duniya a matsayin shugaban kasar Zimbabwe na tsawon wani wa'adin shekaru biyar, kana shugaban da ya fi dadewa a kan karagar mulki a Afirka.

Babban alkalin kasar Godfrey Chidyausiku ne ya rantsar da Mugabe, kafin karfe 12 na rana agogon kasar, inda Mugabe ya ya alkwarin cewa, zai kare martaba da mutunta dokokin kasar, sannan ya yi fatan Allah ya taimake shi wajen sauke nauyin da ke wuyansa.

Ya kuma yi alkawarin cewa, zai kare kundin tsarin mulki da sauran dokokin kasar, kana zai karfafa dukkan abubuwan da za su taimawa wajen ciyar da kasar gaba tare da yin watsi da dukkan abubuwan da za su cutar da kasar Zimbabwe. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China