in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Afirka na yin hadin gwiwa domin moriyar juna
2013-08-08 16:11:16 cri


Tun lokacin da kasar Sin ta kulla dangantaka da kasashen Afirka, wannan dangantaka take ta bunkasa zuwa wani sabon matsayi, abin da ya sa masu sharhi suka bayyana cewa, wannan dangantaka ta yi babban tasiri ga bangarorin biyu, duk da cewa, wasu kasashen yammacin duniya na yi wa wannan kyakkyawar dangantaka bahaguwar fahimta.

Sai dai duk da wannan rashin fahimta da irin wadannan kasashen ke yi wa wannan dangantaka dake tsakanin Sin da Afirka, shugabannin kasar Sin sun jaddada cewa, babban tushen dake tsakanin Sin da Afirka ba zai canja ba.

Alkaluma sun nuna irin tallafi da moriyar da kasashen Afirka suka samu daga wannan dangantaka a bangarori daban-daban kamar su al'adu, ilmi, makamashi, sufuri, tattalin arziki, kiwon lafiya, fasahohin aikin gona da dai sauransu.

Misali na baya-bayan nan, shi ne bashi da tarin yarjeniyoyin da Najeriya ta kulla da gwamnatin kasar Sin yayin ziyarar da shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya kawo kasar Sin a watan Yulin shekarar 2013.

Saboda muhimmancin wannan dangantaka tsakanin bangarorin biyu, har ta kai ga kafa dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, abin dake kara nuna karfafa wannan dangantaka mai tarin alheri ga sassan biyu.

Daga karshe masu fashin baki na cewa, muddin ana bukatar cin gajiyar wannan dangantaka yadda ya kamata, wajibi ne bangarori biyu su mutunta alkawuran da suka cimma, mutunta juna, ta yadda kwalliya za ta biya kudin sabulu a bangarori gwamnatoci da al'ummomin sassan biyu. (Ibrahim Yaya, Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China