in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Angola da Aljeriya na shirin karfafa hadin gwiwa a fannin albarkatun mai
2013-07-10 09:59:59 cri

Mahukuntan kasashen Angola da na Aljeriya sun amince da kafa wata tawagar masana, da za ta tsara managarcin shirin bunkasa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannin albarkatun man fetir.

Da yake karin haske don gane da wannan batu, jim kadan da kammala ganawar wakilan bangarorin biyu ranar Talata 9 ga wata, ministan albarkatun mai na kasar Angola Jose Botelho de Vasconcelos, ya ce, kasarsa ta yanke shawarar bunkasa hadin gwiwar ne, ganin yadda Aljeriya ta rigaya ta yi nisa a wannan fanni.

Vasconcelos ya kara da cewa, dole ne kasar tasa ta yi koyi da irin kwarewar da Algeria ke da ita a dukkanin fannonin haka da sarrafa albarkatun mai. Daga nan sai ministan ya tabbatar da batun sanya hannu kan yarjejeniyar musayar fasaha tsakanin cibiyoyin horaswa a fannin na mai tsakanin kasashen biyu, shirin, a cewarsa, zai mai da hankali sosai ga muhimman kwasa-kwasai da kasashen ke bukatar samun kwararru a cikinsu. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China