in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Afirka ta tsakiya ya alkawarta kafa sabuwar gwamnati nan da kwanaki 3
2013-06-02 15:58:20 cri
A ranar Asabar 1 ga watan Yunin nan da muke ciki ne shugaban kasar Afirka ta tsakiya na wucin gadi Michel Djotodia, ya bayyana cewa nan da kwanaki 3 masu zuwa, za a kafa sabuwar gwamnati a kasar, matakin da ya ce zai kawo karshen matsalolin siyasa dake addabar kasar.

Djotodia ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da shugaban kasar Congo Denis Sassou Nguesso, a garin Oyo dake arewacin kasar ta Congo. Har ila yau shugaban ya ce kafa sabuwar gwamnati na cikin manyan ayyukan da aka dorawa firaministan wucin gadin kasar Nicolas Tiangaye nauyin aiwatarwa. Ban da batun kafa sabuwar gwamnatin, shugaba Djotodia ya ce akwai shirin jibge rundunonin soji a dukkanin lardunan kasar, tare da batun kwance damarar yaki, musamman a helkwatar kasar dake birnin Bangui, matakin da ake sa ran kammalawa nan da makwannin biyu ko uku masu zuwa. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China