in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jirgin saman soji ya fado a kudancin Najeirya
2013-05-10 10:53:23 cri

Kafofin sufurin saman Najeriya sun bayyana cewa, wani jirgin saman soji ya fado a cibiyar sojin sama a jihar Rivers dake kudancin kasar ranar Alhamis da rana.

Kafofin da ba su so a bayyana sunayensu ba sun bayyana wa kamfanin dillancin labaran kasar Sin, Xinhua cewa, jami'ai ba su tantance wadanda hatsarin ya ritsa da su ba, bayan da jirgin ya sauka a filin jiragen saman soji a garin Patakwal, ya kuma kama da wuta.

Zuwa yanzu dai mahukuntan sojin Najeriya sun ki cewa komai dangane da hatsarin ga 'yan jarida.

An samu aukuwar wannan hatsari ne a Najeriya ranar Alhamis, sa'o'i 72 bayan da wani jirgin sama shi ma mallakar sojin saman Najeriya, ya fado ranar Litinin a Niamey, babban birnin kasar Nijar, wanda ya yi sanadin rasuwar rayukan matuka jirgin guda biyu, ko da yake aikin da jirgin yake lokacin da ya fado bai shafi na yaki ba.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China