in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta yi kokarin ciyar da shawarwarin shimfida zaman lafiya da ake yi tsakanin Palesdinu da Isra'ila gaba
2013-05-06 19:23:26 cri
A ranar Litinin 6 ga wata, Li Keqiang, firaministan kasar Sin ya gana da Mahmoud Abbas, shugaban kasar Palesdinu wanda ke yin ziyara a nan Beijing, inda Mr. Li ya bayyana cewa, kasar Sin za ta yi amfani da karfinta wajen ciyar da kokarin yin shawarwarin shimfida zaman lafiya da ake yi tsakanin Palesdinu da Isra'ila gaba ta hanyarta, ta yadda za a iya taimakawa wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya, har ma a duk duniya.

Li Keqiang ya kara da cewa, sabuwar gwamnatin kasar Sin tana mai da hankalinta sosai wajen karfafawa da kuma bunkasa huldar hadin gwiwa irin ta sada zamunta tsakanin kasar Sin da Palesdinu, kuma tana tsayawa tsayin daka kan matsayin nuna goyon baya ga gwagwarmayar neman adalci da jama'ar Palesdinu suke yi.

A nasa bangaren, malam Mahmoud Abbas ya ce, bangaren Palesdinu yana son kara bunkasa hadin gwiwar moriyar juna tsakaninta da kasar Sin, kuma tana maraba da kamfanonin kasar Sin da su zuba jari a Palesdinu. Bugu da kari, malam Abbas ya ce, bangaren Palesdinu na fatan kasar Sin za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa a kokarin kawo zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China