in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU na maraba da maido da harkar mai a Sudan ta kudu
2013-04-13 16:04:01 cri
Shugabar hukumar gudanar da kungiyar hada kan kasashen Afirka (AU) Nkosazana Dlamini Zuma ta yi maraba da maido da harkar mai a kasar Sudan ta kudu da kuma fitar da shi zuwa waje ta cikin bututu mallakar kasar Sudan.

Cikin wata sanarwar da kungiyar ta AU ta bayar ranar Jumma'a, shugabar hukumar gudanar da kungiyar ta lura da cewa wannan ya samar da wata sabuwar alkibla ga daidaita dangantaka tsakanin kasashen Sudan da Sudan ta kudu da kuma bude wani sabon shafi a harkar tattalin arzikin kasashen biyu, wanda ya samu koma baya matuka tun lokacin da aka dakatar da harkar man a shekarar 2012.

Ta nuna gamsuwa kan maido da kokarin hada kai da dagewa ta siyasa a bangaren kasashen biyu na inganta dangantakarsu, inda ta bukace su da su ci gaba kan wannan turba. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China